SDP ta zaɓi Farfesa Sadiq Gombe a matsayin Shugaban Jam’iyya na Ƙasa

Farfesa Sadiq Umar Abubakar Gombe ya zama sabon Shugaban Jam’iyyar SDP na Ƙasa.

An sanar da zaɓensa tare da sauran mambobin Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (NWC) a ranar Asabar yayin babban taron jam’iyyar na ƙasa na shekarar 2026 da aka gudanar a Filin Wasa na Abubakar Tafawa Ɓalewa da ke Bauchi.

Sauran shugabannin da aka zaɓa sun haɗa da Dakta Olu Agunloye a matsayin Sakataren Jam’iyya na Ƙasa; Sanata Dokta Ugochukwu Uba a matsayin Mataimakin Shugaban Jam’iyya na Ƙasa mai kula da Shiyyar Kudu; Hajiya Mariam Maggie Batube a matsayin Ma’ajiya ta Ƙasa; da Barista Joseph Achille Abu a matsayin Sakataren Tsare-tsare na Ƙasa.

 

Post masu alaƙa

An kama wasu mutum 7 da ake zargin ƙusoshin Boko-Haram ne a filin jirgin Katsina

KACRAN ya ti watsi da ƙirƙiro ƴansandan jihohi a Najeriya

INEC na shirin cire NDC daga rajistar jam’iyyun siyasa bayan hukuncin kotu