Muna kashe N150m duk wata kan samar da ruwa —Gwamnan Gombe

Gwamnatin Gombe ta ce tana kashe kimanin Naira miliyan 150 a duk wata domin tabbatar da samar da tsaftataccen ruwan sha ga al’ummar jihar.

Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya ne ya bayyana hakan yayin da yake bayani game da ƙoƙarin da gwamnatinsa ke yi wajen inganta harkar samar da ruwa a birane da karkara.

Ya ce kuɗaɗen na tafiya ne wajen gyara da kula da muhimman kayan aikin ruwa, ciki har da bututan ruwa da suka lalace da kuma na’urorin tace ruwa, domin tabbatar da ci gaba da samar da ruwa mai tsafta.

A cewarsa, gwamnatin jihar ta ɗauki samar da ruwan sha a matsayin ɗaya daga cikin manyan abubuwa da take bai wa fifiko domin inganta lafiyar jama’a da walwalar al’umma.

Post masu alaƙa

Kano: Gini Ya Rufta Kan Mutane 16 Ciki Har Da Yara Shida

Buga fasfo ne aka mayar Abuja, ba karɓarsa ba – Immigration

Hukumar ICPC ta wanke fadar shugaban Najeriya daga zargin kafa hukumar boi