Shettima Ya Isa Landan Don raka Gawar Marigayi Muhammadu Buhari Najeriya

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya isa birnin Landan domin raka gawar marigayi shugaba Muhammadu Buhari da ya rasu a wani asibiti da ke birnin a jiya Lahadi bayan jinya zuwa Najeriya.

Mataimakin shugaban ƙasar ya isa ne tare da rakiyar shugaban ma’aikatan fadar gwamnati Femi Gbajabiamila.

Sun kuma sami tarba daga Ministan harkokin waje Yusuf Tuggar, da Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum a filin jirgin.

Ana sa ran za su dawo Najeriya a yau domin jana’izar tsohon shugaban ƙasar.

Post masu alaƙa

Hadejia ta cika shekaru 120 da cin nasara kan turawan mulkin mallaka na Birtaniya.

NSCDC ta rufe wani gida da ake zargin ana safarar jarirai a Legos.

Rundunar ƴan sandan jihar Zamfara ta kama wanda ake zargi da safarar Alburusai a tankin Babur