Shugaban Kungiyar Kwadago, NLC, Ya Nemi Gwamnatin Tarayya ta Hana Karin Kudin wutar Lantarki

Ƙungiyar ƙwadago ta NLC ta ƙi amincewa da shirin da ake yi na ƙara kuɗin wutar lantarki da kaso 40 ckin 100 nan da 1 ga Yulin 2023.

A sanarwar da ya fitar a Abuja, Kwamared Ajaero ya ce shirin na nuna halin ko-in-kula da rayuwar talakawan Najeriya.

Hukumar kula da farashin lantarki ta ƙasa ce ta amince da ƙarin kuɗin saboda tashin farashin man fetur da kuma karyewar darajar Naira.

Sai dai shugaban na NLC ya buƙaci gwamnati ta hana wannan ƙarin kuɗin wutar.

A cewarsa “dole ne ayi la’akari da adadin wutar da kamfanonin rarraba wutar lantarki ke kawowa da kuma ƙarfin aljihun masu amfani da lantarki wurin biyan kuɗin.

Post masu alaƙa

Manjo Janar Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Yan Bindiga

JIBWIS Gwallaga Sun Ziyarci A Sansanin Alhazai Na Jihar Bauchi Domin Bada Agaji

‘Yan Arewa A Jihohin Kudu Sun Koka kan Tsangwama da Wariya Saboda Matsalolin Tsaro