Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ce sun yi nasarar kwato filaye na triliyoyin Nairori

Kwamitin Rusau na Gwamnan Kano Eng. Abba Kabir Yusuf ya dirarwa gine ginen da aka yi a daura da Titin BUK a hauren wanki.

A jiya Juma’ar nan ne aka ga Hukumar Tsara birane ta jahar kano KNUPDA ta shafa Jan fenti ga Dogayen gine-ginen da aka yi tare da ba su wa’adin kwance gine-ginen bisa hujjar cewa an yi su akan Badala.

Ko a baya baya nan Kungiyoyin Fararen hula irinsu Good Governance and Change Initiative (GGCI) su kiyasta cewa anyi asarar sama da naira Biliyan 150 daga fara rushe gine-ginen da gwamnati ta ce Tsohon Gwamnan Kano Dr Abdullahi Ganduje ya ba da izini yinsu a wuraren da ba su da ce ba.

Sai dai Gwamna Abba Kabir yusuf ya ce daga fara aikin na rusau, gwamnatin kano tai nasarar Kwato filayenta na Triliyoyin naira

Post masu alaƙa

Manjo Janar Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Yan Bindiga

JIBWIS Gwallaga Sun Ziyarci A Sansanin Alhazai Na Jihar Bauchi Domin Bada Agaji

‘Yan Arewa A Jihohin Kudu Sun Koka kan Tsangwama da Wariya Saboda Matsalolin Tsaro