Shugabannin kasashen Turai sun gudanar da taro game da makomar kasar Sin a nahiyar

A yau ne shugabannin ƙasashen Turai za su yi wani muhimmin taro a Brussels, inda ake sa ran batun China na kan gaba cikin muhimman batutuwan da za su tattauna.

Ana sa ran wasu ƙasashe mambobin ƙungiyar za su ga baiken wasu daga cikinsu da ke ci gaba da ɗasawa da Beijing ta fannin tattalin arziki musamman Faransa da Jamus, da suka bayyana aniyarsu ta ci gaba da ƙulla hulɗar kasuwanci mai karfi da Chinar.

Wannan batu dama ya jima yana haifar da rarrabuwar kawuna tsakanin ƙasashen Turan, inda da yawansu ke nuna damuwa game da dangantakar kut da kut da ke tsakanin Beijing ɗin da Rasha.

Wasu daga cikinsu kuwa na fargabar kada dogaron su ga Chinar ya haifar musu da irin raɗadin da suka ji wajen raba gari da Rasha bayan ta ƙaddamar da mamaya a Ukraine

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr