Shugabannin kasashen Turai sun gudanar da taro game da makomar kasar Sin a nahiyar

A yau ne shugabannin ƙasashen Turai za su yi wani muhimmin taro a Brussels, inda ake sa ran batun China na kan gaba cikin muhimman batutuwan da za su tattauna.

Ana sa ran wasu ƙasashe mambobin ƙungiyar za su ga baiken wasu daga cikinsu da ke ci gaba da ɗasawa da Beijing ta fannin tattalin arziki musamman Faransa da Jamus, da suka bayyana aniyarsu ta ci gaba da ƙulla hulɗar kasuwanci mai karfi da Chinar.

Wannan batu dama ya jima yana haifar da rarrabuwar kawuna tsakanin ƙasashen Turan, inda da yawansu ke nuna damuwa game da dangantakar kut da kut da ke tsakanin Beijing ɗin da Rasha.

Wasu daga cikinsu kuwa na fargabar kada dogaron su ga Chinar ya haifar musu da irin raɗadin da suka ji wajen raba gari da Rasha bayan ta ƙaddamar da mamaya a Ukraine

Post masu alaƙa

Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Wata Mata Mai Shekaru 30 Da Katunan ATM 88

Abubuwa shida da suka sauya tun bayan zaɓen Najeriya na 2023

Kanawa mazauna Abuja sun gudanar da babban taro