Sojoji sun ceto mutum 4 bayan shafe shekara 3 a hannun Boko Haram

Dakarun Sojin Najeriya sun ceto wasu mutane huɗu da ake zargin ’yan ta’addan Boko Haram, sun yi garkuwa da su tare da tsare su na tsawon shekaru uku a Jihar Borno.

Sojojin sun ceto su ne da misalin ƙarfe 6 na safiyar ranar 21 ga watan Agusta, yayin wani samame da suka kai kusa da ƙauyen Kauwa, da ke Ƙaramar Hukumar Kukawa.

Rundunar ta ce an gudanar da aikin ne bayan samun bayanan sirri kan wasu ‘yan ta’adda da ake zargin sun tsere daga yankin.

Kwamandan rundunar, Laftanar Kanar E.E. Ukhun ne, ya jagoranci aikin.

A lokacin da sojojin suka yi wa mutanen tambayoyi, sun bayyana cewa ‘yan ta’adda sun sace su ne daga Ƙaramar Hukumar Mafa kimanin shekaru uku da suka gabata.

Sun ce daga Mafa aka kai su sansanin ‘yan ta’adda da ake kira Dogon Chuku, inda aka tsare su har zuwa lokacin da sojoji suka ceto su.

Bayan ceto su, sojojin sun bai wa mutanen abinci sannan suka fara tantance su.

Post masu alaƙa

Najeriya ta ƙaddamar da yaƙi ta sama kan ƴan fashin daji

Jami’ar Sule Lamido ta ziyarci tashar MUHASA kan shirin bude sashen koyar da aikin jarida

Matafiya sun shafe sa’o’i a cunkoson ababen hawa a hanyar Abuja-Kaduna