• Home  
  • Sojoji Sun Ragargaji Sansanonin Lakurawa
- Babban Labari - Labarai

Sojoji Sun Ragargaji Sansanonin Lakurawa

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya ta ‘Operation Fansan Yamma’ sun tarwatsa sansanoni 22 na ‘yan ta’addan Lakurawa a jihar Sakkwato.

Dakarun rundunar Operation Hadarin Daji sun samu nasarar ceto mutane 24 da aka yi garkuwa da su a Kabugu Lamba da ke karamar hukumar Maru ta jahar Zamfara

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya ta ‘Operation Fansan Yamma’ sun tarwatsa sansanoni 22 na ‘yan ta’addan Lakurawa a jihar Sakkwato.

Hakazalika sojojin sun yi nasarar kashe wasu da dama kuma sun kwato makamai da alburusai.

Mukaddashin babban kwamandan runduna ta 8 kuma kwamandan sashi na 2 na rundunar Fansar Yamma, Birgediya Janar Ibikunle Ajose ne ya bayyana hakan, a lokacin da yake jawabi ga runduna ta musamman da aka tura domin murkushe Lakurawa a jihohin Sakkwato da Kebbi a ranar Juma’a.

Ya ce, idan aka tura wasu rundunar ta musamman, to babu shakka zai kara wa rundunar da ke aiki a yankin ƙwarin gwiwa da kuzari wajen dakile ayyukan ‘yan ta’adda a yankin Arewa maso Yamma baki daya.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai