Home » Sojoji Sun Ragargaji Sansanonin Lakurawa

Sojoji Sun Ragargaji Sansanonin Lakurawa

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Dakarun rundunar Operation Hadarin Daji sun samu nasarar ceto mutane 24 da aka yi garkuwa da su a Kabugu Lamba da ke karamar hukumar Maru ta jahar Zamfara

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya ta ‘Operation Fansan Yamma’ sun tarwatsa sansanoni 22 na ‘yan ta’addan Lakurawa a jihar Sakkwato.

Hakazalika sojojin sun yi nasarar kashe wasu da dama kuma sun kwato makamai da alburusai.

Mukaddashin babban kwamandan runduna ta 8 kuma kwamandan sashi na 2 na rundunar Fansar Yamma, Birgediya Janar Ibikunle Ajose ne ya bayyana hakan, a lokacin da yake jawabi ga runduna ta musamman da aka tura domin murkushe Lakurawa a jihohin Sakkwato da Kebbi a ranar Juma’a.

Ya ce, idan aka tura wasu rundunar ta musamman, to babu shakka zai kara wa rundunar da ke aiki a yankin ƙwarin gwiwa da kuzari wajen dakile ayyukan ‘yan ta’adda a yankin Arewa maso Yamma baki daya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?