APC

Abin da ya sa na koma APC – Gwamnan Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa rikicin cikin gida da kuma shari’o’in da suka dabaibaye tsohuwar jam’iyyarsa ta PDP ne babban dalilan da suka sa ya fice daga jam’iyyar zuwa APC. A ranar Litinin ne gwamnan ya sanar da sauya sheƙarsa daga PDP zuwa jam’iyya mai mulki ta APC a hukumance bayan wani […]

Read more

Gwamnan Adamawa Ahmadu Fintiri ya koma APC

Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya sanar da sauya sheƙarsa zuwa jam’iyyar APC a hukumance. A jawabin da ya yi wa al’ummar jiha a ranar Juma’a, gwamnan ya ce ya ɗauki matakin ne tare da duka mambobin majalisar zartarwarsa da manyan jiga-jigan jam’iyyar adawa ta PDP, kamar yadda jaridun ƙasar suka ruwaito. Sauya shekar […]

Read more

APC ta fara faɗawa tarkon rikici a jihar Kano

Kurar rikici ta fara turnuƙewa a jam’iyyar APC mai mulki a jihar Kano, da ke arewacin Najeriya, makonni bayan sauyin sheƙar gwamna Abba Kabir Yusuf. An fara ganin ƙurar ne a tarukan haɗa kan ‘ya’yan jam’iyyar APC tsoffi da sabbi a cikin wasu ƙananan hukumomin jihar. Shugabancin APC ne ya ba da umarnin gudanar da […]

Read more

APC ta naɗa Masari shugaban babban taronta na ƙasa

Jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya ta maye gurbin gwamnan jihar Imo Hope Uzodinma da tsohon gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari a matsayin shugaban kwamitin babban taronta na ƙasa. Babban sakataren jam’iyyar na ƙasa, Surajudeen Basiru ne ya bayyana haka cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X. Jam’iyyar ta saka ranakun 27 […]

Read more