APC

Ƙungiyoyin PDP 293 sun koma APC a Yobe

A wani gagarumin sauyin siyasa a Jihar Yobe, ƙungiyoyi 293 na Jam’iyyar PDP sun sauya sheƙa zuwa APC a Ƙaramar Hukumar Potiskum.   Sauyin sheƙar wanda shi ne mafi girma a yankin a ’yan kwanakin nan ya samu jagorancin Shugaban PDP na Ƙaramar Hukumar Potiskum, Alhaji Audu Hamisu, wanda aka fi sani da Soja Boy. Masu […]

Read more

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a yankin Ikot Ekpene na jihar Akwa Ibom sun yi watsi da shirin baiwa ɗan takara tikitin kai tsaye domin kujerar majalisar dokokin jihar mai wakiltar Ikot Ekpene/Obot Akara, gabanin zaɓen fidda gwani na jam’iyyar, inda suka bayyana hakan a matsayin saɓawa ka’idojin dimokuraɗiyya. An bayyana matsayar ne […]

Read more

Ko Amupitan ya sauka ko mu ɗauki matakin ban mamaki – ADC

Jam’iyyar ADC mai adawa a Najeriya tace ko Shugaban Hukumar zaɓen ƙasar mai zaman kanta INEC Joash Amupitan ya sauka daga muƙaminsa ko kuma sau ɗauki matakin da zai girgiza kasar. Jam’iyyar ta bayyana haka ne lokacin da take gabatar da wasu sabbin zarge-zarge kan shugaban hukumar. ADC ta soki Amupitan kan tsofaffin bayanansa da […]

Read more

Dan Sarkin Daura ya fito takarar dan Majalisar Wakilai

Muhammad Daha, ɗa ga Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Faruk Umar Faruk, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar Majalisar Tarayya mai wakiltar Baure/Zango a zaɓen 2027. Daha, wanda ke rike da sarautar Danburam na Daura, ya ce matakin ya biyo bayan kiraye-kiraye  daga al’ummarsa da ke son ya wakilce su a Majalisar Tarayya. “Ina […]

Read more

Ƴan majalisar wakilai 8 na Kano sun fice daga NNPP zuwa APC

Ƴan Majalisar Wakilai takwas daga Jihar Kano sun sanar da ficewarsu daga jam’iyyar NPP zuwa jam’iyyar APC, lamarin da ya ƙara girgiza siyasar jihar. Shugaban Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ne ya sanar da sauya sheƙar a hukumance yayin zaman majalisar a yau Talata, bayan karanta wasiƙun da ‘yan majalisar suka aike wa zauren. A cikin […]

Read more

Gawuna ya ajiye muƙamin da Tinubu ya ba shi

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano kuma ɗan takarar gwamnan Jihar na jam’iyyar APC a 2023, Nasiru Yusuf Gawuna, ya ajiye muƙaminsa na Shugaban Hukumar Gudanarwar bankin bayar da lamunin gidaje na Najeriya. Sanarwar da tsohon mataimakin gwamnan ya fitar ta nuna cewa ajiye aikin zai fara ne daga gobe Talata, 31 ga Maris, 2026. A […]

Read more

Sunayen sabbin shugabannin jam’iyar APC

Jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya ta zaɓi sabbin shugabannin da za su jagorance har an da shekaru huɗu masu zuwa. An zaɓi sabbin shugabbnin ne a lokacin babban taron jam’iyyar na ƙasa da aka gudanar ranar Juma’a a Abuja. APC ta sanar da zaɓen Farfesa Nentawe Yilwatda – shugaban riƙon jam’iyyar – a matsayin cikakken […]

Read more

Mataimakin Gwamnan Kano Ya Yi Murabus

Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdussalam Gwarzo ya yi murabus daga muƙaminsa. Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ƙungiyar Kwankwasiyya ta fitar, wadda kakakinta Dr Habibu Sale Mohammed ya fitar da yammacin ranar Juma’a. Ya ce mataimakin gwamnan ya ɗauki matakin ne domin tabbatar da zaman lafiya a jihar Kano da tabbatar […]

Read more