Muhammad Daha, ɗa ga Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Faruk Umar Faruk, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar Majalisar Tarayya mai wakiltar Baure/Zango a zaɓen 2027.
Daha, wanda ke rike da sarautar Danburam na Daura, ya ce matakin ya biyo bayan kiraye-kiraye daga al’ummarsa da ke son ya wakilce su a Majalisar Tarayya.
“Ina sanar da magoya bayana cewa na amince da kiran da aka yi min. Na yanke shawarar tsayawa takarar kujerar majalisar wakilai domin wakiltar Baure/Zango a zaɓen 2027. Ina kuma roƙon magoya bayana da su guji duk wani abu da zai iya zama raini ko cin mutunci ga kowa a cikin goyon baya gare ni,” in ji shi.
Sai dai bai bayyana jam’iyyar da zai tsaya a ƙarƙashinta ba, lamarin da ake ganin na iya zama dabara. Wasu majiyoyi sun ce akwai yiwuwar ya tsaya a ƙarƙashin APC ko kuma ADC.
Muhammad Daha Umar Faruk ya shahara wajen tallafa wa matasa da kuma gudanar da ayyukan ci-gaban al’umma, musamman a fannin wasanni a yankin.