Jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya ta zaɓi sabbin shugabannin da za su jagorance har an da shekaru huɗu masu zuwa.
An zaɓi sabbin shugabbnin ne a lokacin babban taron jam’iyyar na ƙasa da aka gudanar ranar Juma’a a Abuja.
APC ta sanar da zaɓen Farfesa Nentawe Yilwatda – shugaban riƙon jam’iyyar – a matsayin cikakken shugabanta na ƙasa.
Haka kuma jam’iyyar ta tabbatar da Surajudeen Basiru a matsayin cikakken sakataren jam’iyyar na ƙasa.
An dai zaɓi mafi yawan jagororin jam’iyyar ta hanyar masalaha, kamar yadda jam’iyyar ta fi bai wa fifiko.
Ga jerin sunayen sabbin jagororin jam’iyyar:
- Shugaban Jam’iyya na ƙasa: Farfesa Nentawe Yilwatda
- Mataimakin Shugaba (Arewa): Ali Bukar Dalori
- Mataimakin Shugaba (Kudu): Dr. Benjamin Obi Nwoye
- Sakataren Jam’iyyar na ƙasa: Sen. Surajudeen Ajibola Basiru
- Mataimakin Sakatare: Prof. AbdulKarim Abubakar Kana
- Babban Lauyan Jam’iyya: Murtala Aliyu Kankia
- Babban Ma’aji na ƙasa: Uguru Mathew Ofoke
- Babban Sakataren Kuɗi: Amb. Haruna Ginsau
- Babban Sakataren tsare-tsare: Muhammad Sulaiman Argungu, OFR
- Sakataren Walwawa: Donatus Enyinnah Nwankpa
- Sakataren Yaɗa Labarai: Felix Morka
- Babban Mai Binciken kuɗi: Sen. Abubakar Maikafi
- Shugabar Mata: Dr Mary A. Idele
- Shugaban Matasa: Dayo Israel