Tag: labarai

Labarai

Hukumomin Nijar Sun Ƙi bude iyakokinsu da Najeriya

Rahotannin na nuni da cewa har zuwa wannan lokaci hukumomin ƙasar Nijar ba su kai ga buɗe iyakokinsu ba duk kuwa da umarnin da shugaba Bola Ahmad Tinubu ya bayar, a ranar 13 ga watan Maris na wannan shekara, na janye takunkumin da aka ƙaƙaba wa Nijar. Tun bayan umarnin na shugaban ƙasa ne, shugabar […]

Kaduna
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Sace Mutane 8 a Kaduna

Wasu ‘yan bindiga a sanyin safiyar nan sun kai wani sabon hari garin Dogon-noma da ke ƙaramar hukumar Kajuru da ke jihar Kaduna. Wannan hari na zuwa ne kwanaki uku bayan kashe wani mutum ɗaya da yin garkuwa da mutane 8 a garin Banono Angwaku  da ke ƙaramar hukumar ta Kajuru. Tsohon shugaban ƙaramar hukumar, […]

kankara
Labarai

Ramadan: Ƙanƙara Ta Zama ‘Yar Sarki a Kano

A yayin da ake kai azumi na shida a yau, al’umma na cigaba da nuna damuwa game da farashin ƙanƙara wanda sukan yi amfani da ita domin sanyaya abin sha a lokacin buɗa baki. Su ma masu sana’ar sun bayyana wa abokiyar aikinmu irin ƙalubalen da suke fuskanta, musamman a lokacin da ake fama da […]

Nkiruka Onyejeocha
Labarai

Gwamnatin tarayya ta cika alƙawuran da ta yi ~ Ministar Ƙwadago

Ministar ƙwadago da ayyukan yi Nkiruka Onyejeocha, ta ce gwamnatin tarayya ta yi nasarar cika alƙawuran da ta yi wa ƙungiyar ƙwadago a watan Oktoban bara da kashi 90 cikin 100.   Ta ce yanzu lokaci ne da ya kamata ƙungiyoyin ƙwadago su tallafa wa gwamnatin tarayya.   Minstar dai ta bayyana hakan ne a […]

Labarai

Kano: Gamayyar Shugaban ‘Yan Kasuwa Ya Yaba wa Kwamishinan ‘Yan Sanda

Shugaban gamayyar kasuwannin Sabon Gari ta Abubakar Rimi da Singa da Kasuwar Galadima da kuma ƙungiyar Kawo Ƙarshen Fatara a jihar Kano, wato Kano Alternative for Poverty Eradication sun yaba wa kwamishinan ‘yan sandan jihar nan, CP Mohammed Usaini Gumel saboda gudunmowar da yake bayarwa wajen ci gaban matasa da wanzar da zaman lafiya a jihar […]

Christopher Musa
Babu Rukuni

Rundunar Sojin Najeriya ta gargaɗi masu kiran juyin mulki

Rundunar sojin Najeriya ta gargaɗi mutanen da ke yin kira da a yi juyin mulki a ƙasar nan saboda tsadar rayuwa da ake ciki. Wannan na zuwa ne a lokacin da ƙasar nan ke cigaba da fuskantar matsaloli da suka shafi tattalin arziƙi da tsaro waɗanda suka haifar da zanga-zanga a kwanakin baya a wasu […]

Dr Tunji Alausa
Labarai

Lafiya: An buƙaci gwamnatin tarayya ta tallafa wa masu cutar daji

Ƙaramin Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a, Dr Tunji Alausa, ya ce gwamnnatin tarayya na kan haɗa guiwa da kamfanonin haɗa magunguna domin rage tsadar da magungunan cutar kansa ke yi da ma tsarin ba da kulawa a  ƙasar nan. Ministan ya bayyana hakan ne a yayin taron Ranar Masu Fama da Cutar Kansa ta Duniya […]

KANO
Labarai

Kano: Wata Kungiya ta Buƙaci a Dawo da Sarkin Kano 14 Kan Karagarsa

Wata ƙungiya mai suna ‘Yan Dangwalen Jihar Kano, sun buƙaci majalisar dokokin jihar Kano, da ta dawo da Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sunusi na II, kan karagarsa tare da rushe sabbin masarautun da aka samar.   A ranar 3 ga watan Maris, 2020 ne, gwamnan Kano na wannan lokaci, gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ne ya sauƙe sarkin […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai