Nigeria

Daraktan yaɗa labaran DHQ Manjo Janar Samaila Uba, ya bayyana cewa a yaƙin haɗin gwiwa da dakarun Najeriya da kuma sojojin Amurka na AFRICOM suna cin galabar ‘yan ISIS. Manjo Janar Sama’ila Uba ya bayyana hakan ne a jiya Talata a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja.

Read more

Najeriya na ƙara sa ido bayan ɓarkewar Ebola a Congo

Hukumar Daƙile Yaɗuwar Cututtuka a Najeriya, NCDC ta ce duk da cewa ba a samu ɓullar cutar Ebola ba a ƙasar, tana ƙarfafa matakai don sa ido sakamakon mutuwar mutum 88 a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo da kuma samun mutum guda da aka bayar da rahoton ya kamu da cutar a Uganda. Cikin wata sanarwa da […]

Read more

Adadin ɗabilan da aka sace daga Borno sun kai 50

Bayanan da ke fitowa daga Najeriya na cewa fiye da ɗalibai 50 ne aka bayar da rahoton garkuwa da su a wasu hare-hare da aka kai wa makarantu a yankin arewa maso gabashin ƙasar aranar Juma’a Rahotonni na cewa mafi yawan yaran ƴan tsakanin shekara biyu zuwa biyar ne, waɗanda aka sace daga makarantun nazare. […]

Read more

Najeriya ta ƙarfafa ƙawancen tsaronta da Amurka

Najeriya ta Amuka sun amince da ƙarfafa haɗin kan tsaro tsakaninsu domin yaƙi da ta’addanci. Cikin wata sanarwa da kakain shugaban ƙasar Bayo Onanuga ya fitar, ya ce an cimma hakan ne a ganawar da mai taimaka wa shugaban ƙasar kan harkokin tsaro Mallam Nuhu Ribadu ya yi da mataimakin shugaban Amurka, JD Vance da […]

Read more

EFCC ta ayyana neman Sadiya Farouq ruwa a jallo

Hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya ta ayyana neman tsohowar ministar jin ƙai ta ƙasar, Sadiya Umar Farouq ruwa a jallo. Cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na internet, ta ce tana neman tsohuwar ministar bisa zarge-zargen laifukan haɗa baki domin aikata laifuka da amfani da ofishi […]

Read more

Jam’iyyar NDC na gudanar da babban taronta na ƙasa

Jam’iyyar hamayyar ta NDC a Najeriya na gudanar da babban taronta na ƙasa domin zaɓen sabbin shugabanninta. Matakin na zuwa ne mako guda bayan da manyan jiga-jigan siyasar ƙasar biyu, Peter Obi da Kwankwaso suka sanar da komawa cikinta. Ɗaruruwan magoya bayan jam’iyyar ne suka taru a harabar wurin gudanar da taron a Abuja. Akwai […]

Read more