Tinubu Ya Aiyana Dokar Ta Baci Kan Tsaro A Nijeriya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro a faɗin ƙasar, yana mai bayar da umarnin ɗaukar ƙarin jami’an ‘yansanda da na soja.

Shugaban wanda ya bayar da umarnin yayin wani jawabi a fadarsa, ya bai wa rundunar ‘yansandan ƙasar umarnin ɗaukar ƙarin jami’ai 20,000.

Ya ce adadin sababbin jami’an da za a ɗauka yanzu ya zama 50,000, bayan umarnin da ya bayar ranar Lahadi na ɗaukar 30,000.

Ɗaya daga cikin mai magana da yawun fadar shugaban ƙasa, Abdulaziz Abdulaziz, ya faɗa wa BBC cewa dokar na nufin ɗaukar matakan gaggawa domin shawo kan matsalar tsaro a faɗin Najeriya.

Kazalika, shugaban ya bai wa hukumar ‘yansandan farin kaya ta DSS umarnin ɗaukar ƙarin jami’ai a rundunar kare dazuka ta Forest Guard.

Shugaba Tinubu ya kuma umarci DSS ta aika dakarun Forest Guard “domin zaƙulo ‘yanta’adda da ‘yanfashi daga dazuka”.

“Babu wani sauran gidan ɓuya ga miyagu,” in ji shi kamar yadda wata sanarwa daga fadar shugaban ta bayyana.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda