Tinubu Ya Miƙa Sunan Dambazau A Matsayin Ambasada

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tura ƙarin sunan mutum 4 ɗoriya a kan waɗanda aka fitar a baya zuwa ga majalisar dattawa domin a tantance su a matsayin jakadun ƙasar da za a tura ƙasashen waje.

Mutum huɗu da Tinubu ya tura su ne: Ibok-Ete Ekwe Ibas, tsohon shugaban riƙon-ƙwarya na jihar Rivers da tsohon ministan harkokin cikin gida Abdulrahman Dambazau.

Sauran kuma su ne Sanata Ita Enang da tsohon gwamnan jihar Imo Chioma Ohakim.

Yanzu dai jimilla shugaban ya tura sunan mutum 65 ke nan da yake buƙatar majalisar ta tantance, inda ake sa ran da zarar an tantance su, zai sanar da ƙasashen da za a tura su.

Post masu alaƙa

Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad Ya ce suna nema Jam’iyyar da za su shiga amma banda APC

Ƴan bindiga sun sace basarake da matarsa a jihar Kwara

Tsohon shugaban hukumar kwallon kafa ta Najeriya Galadima ya rasu