Tinubu ya nemi tura ƙarin jakadu 32 zuwa ƙasashen waje

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya miƙa wa majalisar dattawa sunayen mutum 32 da yake son turawa a matsayin jakadun ƙasar zuwa ƙasashen waje.

Wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta fitar a yau Asabar ta ce shugaban ya nemi majalisar ta gagaggauta tantancewa da amincewa da mutanen.

Sunayen sun ƙunshi Femi Fani-Kayode, tsohon ministan sufurin jiragen sama, da Reno Omokri, tsohon mai taimaka wa shugaban ƙasa na musamman.

A ranar Alhamis ne Tinubu ya nemi majalisar ta amince da tura jakadu zuwa Amurka da Ingila da Faransa.

Fiye da shekara biyu kenan da gwamnatin APC ƙarƙashin Tinubu ta yi wa jakadun ƙasar kusan 109 kiranye kuma tun daga lokacin wakilai ne ke tafiyar da ofisoshin jakadancin Najeriya a ƙasashen waje.

1. Barrister Ogbonnaya Kalu (Abia)
2. Reno Omokri (Delta)
3. Prof. Mahmood Yakubu (Bauchi)
4. Erelu Bisi Angela Adebayo (Ekiti)
5. Ifeanyi Ugwuanyi (Enugu)
6. Tasiu Musa Maigari (Katsina)
7. Yakubu N. Gambo (Plateau)
8. Prof. Nora Ladi Daduut (Plateau)
9. Otunba Femi Pedro (Lagos)
10. Chief Femi Fani-Kayode (Osun)
11. Barr. Nkechi Linda Ufochukwu (Anambra)
12. Fatima Florence Ajimobi (Oyo)
13. Lola Akande (Lagos)
14. Grace Bent (Adamawa)
15. Dr. Victor Okezie Ikpeazu (Abia)
16. Senator Jimoh Ibrahim (Ondo)
17. Ambassador Paul Oga Adikwu (Benue)

18. Enebechi Monica Okwuchukwu (Abia)
19. Yakubu Nyaku Danladi (Taraba)
20. Miamuna Ibrahim Besto (Adamawa)
21. Musa Musa Abubakar (Kebbi)
22. Syndoph Paebi Endoni (Bayelsa)
23. Chima Geoffrey Lioma David (Ebonyi)
24 Mopelola Adeola-Ibrahim (Ogun)
25 Abimbola Samuel Reuben (Ondo)
26. Yvonne Ehinosen Odumah (Edo)
27. Hamza Mohammed Salau (Niger)
28. Ambassador Shehu Barde (Katsina)
29. Ambassador Ahmed Mohammed Monguno (Borno)
30. Ambassador Muhammad Saidu Dahiru (Kaduna)
31. Ambassador Olatunji Ahmed Sulu Gambari (Kwara)
32. Ambassador Wahab Adekola Akande (Osun)

Post masu alaƙa

Hadejia ta cika shekaru 120 da cin nasara kan turawan mulkin mallaka na Birtaniya.

NSCDC ta rufe wani gida da ake zargin ana safarar jarirai a Legos.

Rundunar ƴan sandan jihar Zamfara ta kama wanda ake zargi da safarar Alburusai a tankin Babur