Tinubu ya yi alhinin rasuwar ɗan kasuwar Kano Bature Abdulaziz

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhini da jimami kan rasuwar fitaccen ɗan kasuwa kuma jagoran al’ummar ’yan kasuwa a Jihar Kano, Alhaji Bature Abdulaziz, wanda ya rasu a ƙarshen mako.

Cikin wata sanarwa da fadarsa ta fitar, Tinubu ya miƙa ta’aziyyarsa ga al’ummar ’yan kasuwa a Kano da iyalan marigayin, da gwamnatin Jihar Kano bisa wannan babban rashi.

Shugaban ya bayyana mutuwarsa a matsayin babban rashi ba ga al’ummar kasuwancin Kano kaɗai ba, har ma da sassa da dama na Najeriya, duba da tasirinsa a harkokin kasuwanci.

A cewar Tinubu, marigayi Bature Abdulaziz ya taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa harkokin kasuwanci a ƙasar, inda ya shugabanci ƙungiyoyi da dama masu alaƙa da kasuwanci.

Kafin rasuwarsa, shi ne Shugaban Ƙungiyar ’Yan Kasuwa ta Najeriya tare da bayar da gudunmawa mai yawa wajen haɗa kan ’yan kasuwa a faɗin ƙasa.

Tinubu ya kuma tuna da irin goyon bayan da marigayin ya ba shi a lokacin yaƙin neman zaɓensa a shekarar 2023, tare da rawar da ya taka wajen inganta haɗin kan ƙasa da kishin ƙasa ta hanyar ƙungiyar Patriotic Elders Network for Peace (PENP) da ya kafa.

Post masu alaƙa

Ba za mu buɗe Hormuz ba sai Amurka ta buɗe tashar ruwanmu – Iran

Jirgin ‘yan cirani ya kife a tekun Libiya

Da buƙatar samar da takin zamani ga manoman Najeriya – MDD