BOLA

Tinubu ya cire ministan kuɗi da na gidaje

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yi wasu sauye-sauye a majalisar ministocin ƙasar, inda ya cire ministan kuɗi, Wale Edun da ministan gidaje, Ahmed Musa Dangiwa. A wata sanarwa da sakataren gwamnatin ƙasar, Sanata George Akume ya fitar, ya ce an buƙaci ministan kuɗin ya miƙa aiki ga ƙaramin ministan kuɗin ƙasar, Taiwo Oyedele, wanda zai […]

Read more

Shettima ya kai ziyara Kwara bayan mummunan harin jihar

Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya kai ziyarar jaje zuwa jihar Kwara inda mahara suka kashe gomman mutane cikin makon nan. Cikin wata sanarwa da fadarsa ta fitar ta ce Shettima ya kai ziyarar ce bisa umarnin shugaban ƙasar Bola Tinubu. “Shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya umarci mataimakinsa ya kai ziyarar jaje jihar da kuma […]

Read more

Tinubu ya yi tir da kisan mace da ƴaƴanta shida a Kano

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kakkausar suka kan kisan gilla da aka yi wa wata matar aure mai suna Fatima Abubakar, da ƴaƴanta shida a unguwar Chiranci da ke Jihar Kano. Cikin wata sanarwa da fadarsa ta fitar, Shugaba Tinubu ya bayyana lamarin a matsayin mummunan rashin imani da rashin tausayi, wanda ya […]

Read more

Tinubu ya yi alhinin rasuwar ɗan kasuwar Kano Bature Abdulaziz

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana alhini da jimami kan rasuwar fitaccen ɗan kasuwa kuma jagoran al’ummar ’yan kasuwa a Jihar Kano, Alhaji Bature Abdulaziz, wanda ya rasu a ƙarshen mako. Cikin wata sanarwa da fadarsa ta fitar, Tinubu ya miƙa ta’aziyyarsa ga al’ummar ’yan kasuwa a Kano da iyalan marigayin, da gwamnatin Jihar […]

Read more

Tinubu ya buƙaci sojoji su ci gaba da martaba dimokuraɗiyya

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya buƙaci rundunar sojin Najeriya da su kasance masu ladabi, haɗin kai da kuma martaba dimokuraɗiyya. Ya bayyana sojoji a matsayin ginshiƙin wajen haɗin kan ƙasa da kuma kare dimokuradiyyar Najeriya. Shugaban ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa sojoji domin tabbatar da zaman […]

Read more

An haramta sana’ar bola-jari a Gombe

Gwamnatin Gombe ta haramta sana’ar bola jari a duk faɗin jihar, bisa abin da ya kira barazanar tsaro da kuma zargin sana’ar da ƙarfafa ayyukan laifi. An yanke wannan shawara ne a wani taron Majalisar Tsaro na musamman da gwamnatin jihar ta gudanar tare da manyan jami’an tsaro, ƙarƙashin jagorancin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, domin […]

Read more