Home » Tsoffin ‘Yan Sanda 500 Sun Mutu Suna Neman Haƙƙinsu

Tsoffin ‘Yan Sanda 500 Sun Mutu Suna Neman Haƙƙinsu

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga Muhammad Auwal Suleiman da Hauwa Umar Tela

Ƙungiyar tsoffin ‘yan sandan Najeriya (REPON) reshen jihar Bauchi ta bayyana cewa mambobinta guda 500 sun mutu ba a biya su hakkinsu na kammala aiki ba. 

Haka zalika REPON ta bayyana rashin jin daɗinta bisa gaza aiwatar da ƙudurin neman a kafa hukumar da zata lura da hakkokin tsofaffin ‘yan sandan Najeriya dake gaban majalisar wakilai tun shekarar 2012.

Waɗannan bayanai na ƙunshe ne a cikin wani jawabi da sakataren ƙungiyar tsofaffin ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Bauchi ASP John Iliya mai ritaya ya yi wa ‘yan jarida.

Ya ce “ mun gaji da gafara sa ba mu ga ƙaho ba, lokaci ya yi da za a ɗauki mataki”

Sakataren ya ce, sun yi zanga-zangar lumana a ƙofar majalisar wakilan Najeriya dake Abuja ranar 21 ga Watan Mayu, 2024.

A lokacin wannan zanga-zangar, shugaban kwamitin harkokin ‘yan sandan Najeriya a zauren majalisar dattawan Najeriya, sanata Ahmed Abdulkadir Malam Madori da wasu abokan aikinsa sun musu alƙawari cewa za a dubi lamarin su a watan Satumba.

Ya ce, har a ranar 2 ga watan Oktoba, ba a taɓa ambaton maganar tsofaffin ‘yan sanda ba a majalisar, musamman ma waɗan da suka fito daga jihar Bauchi.

ASP John Iliya mai ritaya ya ce idan har majalisar bata tuno da su ta yi abin da ya dace ba, to ba shakka za su fito su sake yin zanga-zanga.

Ya ce, ɗaya daga cikin manyan buƙatun da suka gabatar wa majalisar wakilan Najeriya shine fatan a cire ‘yan sandan Najeriya daga tsarin fansho na CPS, a dawo a ƙirƙiri hukuma mai zaman kanta da za ta sa ido akan harkokin haƙƙoƙinsu.

Hakan a cewar sa, zai taimaka wajen bai wa ‘yan sandan dama su lura da haƙƙinsu yadda ya kamata.

REPON ta bayyana rashin jin daɗinta dangane da yadda majalisar ta gaza tattaunawa akan batun da ya shafi tsofaffin ‘yan sandan.

Ƙungiyar ta ƙalubalanci majalisar bisa yadda suka gaggauta sanya hannu akan ƙudurin neman a tsawaita wa shugaban rundunar ‘yan sandan Najeriya shekarun aiki bayan lokacin ritayarsa ta yi. Amma aka manta da buƙatar da suka miƙa.

A ƙarshe sun buƙaci majalisa ta gaggauta duba ƙudurin da suka aika mata, ko kuma a fuskanci mummunar zanga-zanga.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?