Tsohon Hadimin shugaba Buhari Ya Zama Mataimakin Shugaban Jaridar The Sun

Tsohon Mai Ba Wa Shugaban Ƙasa Shawara a Kan Harkokin Yaɗa Labarai, Femi Adesina, ya ce, ya shirya karɓar mukamin mataimakin shugaban Jaridar The Sun, wanda ake sa ran zai fara aiki a ranar 1 ga watan Satumba.

A baya dai Femi Adesina ya riƙe muƙamin Edita a Kamfanin Jridar ta The Sun, a matakai daban-daban.

Wannan bayani, ya fito ne daga bakin Adesinan a yayin da yake tattaunawa da manema labarai, Inda ya bayya na cewar, Shugaban Kamfanin, Senator Orji Kalu,  ya tabbatar da ba shi muƙamin.

Adesina ya ce a yayin da ya bayyana aniyarsa ta barin gidan jaridar a baya, Kalu ya shawarce shi a kan kada ya rubuta takardar barin aiki.

A maimakon haka sai ya ba shi damar ya je ya riƙe mukaminsa na Gwamnati, daga baya bayan ya gama, ya iya dawowa.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr