Tsohon Hadimin shugaba Buhari Ya Zama Mataimakin Shugaban Jaridar The Sun

Tsohon Mai Ba Wa Shugaban Ƙasa Shawara a Kan Harkokin Yaɗa Labarai, Femi Adesina, ya ce, ya shirya karɓar mukamin mataimakin shugaban Jaridar The Sun, wanda ake sa ran zai fara aiki a ranar 1 ga watan Satumba.

A baya dai Femi Adesina ya riƙe muƙamin Edita a Kamfanin Jridar ta The Sun, a matakai daban-daban.

Wannan bayani, ya fito ne daga bakin Adesinan a yayin da yake tattaunawa da manema labarai, Inda ya bayya na cewar, Shugaban Kamfanin, Senator Orji Kalu,  ya tabbatar da ba shi muƙamin.

Adesina ya ce a yayin da ya bayyana aniyarsa ta barin gidan jaridar a baya, Kalu ya shawarce shi a kan kada ya rubuta takardar barin aiki.

A maimakon haka sai ya ba shi damar ya je ya riƙe mukaminsa na Gwamnati, daga baya bayan ya gama, ya iya dawowa.

Post masu alaƙa

‘Yan Arewa A Jihohin Kudu Sun Koka kan Tsangwama da Wariya Saboda Matsalolin Tsaro

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama