Yadda Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ma’aikacin Jami’a A Kano 

Masu ƙwacen waya sun kashe wani ma’aikacin Jami’ar Northwest da ke Kano, Buhari Imam, ta hanyar daɓa masa wuƙa a ciki. 

Rahotanni sun bayyana cewa ɓarayin sun ritsa shi ne a yankin unguwar Sheka da ke karamar hukumar Kumbotso, inda suka sossoke shi da wuka a ciki kuma suka kwace wayarsa, a ranar Laraba.

Kafar yaɗa labarai ta BBC ta ruwaito cewa malamin ya rasu bayan da aka garzaya da shi Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, a ranar Juma’a.

Kwamared Bashir Muhammad Shugaban ƙungiyar ma’aikatan jami’ar (NASU), wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin ya buƙaci gwamnatin Jihar Kano da sauran hukumomi da su ɗauki tsattsauran mataki a kan kisan.

Post masu alaƙa

JIGAWA: ‘Yan siyasa sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya gabanin zaben 2027

Sarkin Gumel Ahmed Muhammad Sani II ya rasu

Yan sanda sun kama mutane 79 tare da kwato kwayoyi da makamai a bikin Takutaha a Kano.