Home » Yadda Za A Magance Matsalar Ƙwacen Waya- CP Wakili (Singham)  

Yadda Za A Magance Matsalar Ƙwacen Waya- CP Wakili (Singham)  

Tsohon Kwamishinan ’yan sandan Najeriya a Jihar Kano CP Muhammad Wakili mai ritaya (Singham) ya ce samar wa matasa aiki zai iya magance balahirar ƙwacen waya.

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Tsohon Kwamishinan ’yan sandan Najeriya a Jihar Kano CP Muhammad Wakili mai ritaya (Singham) ya ce samar wa matasa aiki zai iya magance balahirar ƙwacen waya.

Cp Wakili mai ritaya ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi da kafar yaɗa labarai ta TRT.

Tsohon Kwamishinan ya yi wannan jawabin ne a daidai lokacin da ake cigaba da asarar rayuka a sassan Arewacin Najeriya sakamakon ƙwacen waya.

A kasa da mako guda, rahotanni sun bayyana cewa masu ƙwacen waya sun halaka wani soja a kan gadar Kawo jihar Kaduna, sun kuma halaka wani a jihar Gombe.

Ƙwacen waya da faɗan daba ya jima yana janyo asarar rayuka a jihar Kano da sassan Arewacin Najeriya.

Sai dai masana da dama baya ga CP Wakili mai ritaya sun sha bayyana rashin aikin yi tsakanin matasa a matsayin abin da ke kara jefa mutane cikin bala’in ƙwacen waya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?