Zamfara: ‘Yan bindiga sun sace daliban da ba san adadinsu ba

Rahotanni  daga jihar Zamfara na cewa wasu ƴan bindiga sun kai hari gidajen kwanan ɗaliban Jami’ar dake Gusau, tare da sace ɗaliban da  har yanzu ba a tantance adadinsu ba.

Lamarin dai ya faru ne da asubahin Juma’ar nan, inda rahotanni ke cewa maharan sun kutsa gidajen kwanan ɗalibai uku a unguwar Sabon Gida da ke maƙwaftaka da jami’ar.

Bayanan na cewa ƴan bindigar sun samu nasarar kwashe kusan dukkanin ɗaliban da ke zaune a gidajen da ke daura da jami’ar.

Har yanzu dai hukumomi ba su yi ƙarin bayani kan lamarin ba.

Post masu alaƙa

Kwamitin zaman lafiya ya gana da yan sandan Kano kan zaɓen 2027.

An kashe kwamandojin ’yan bindiga biyu a Katsina

Yan Sandan a Kano sun kama mutane 244, ciki har da 117 da ake zargi da fadan daba.