‘Yan Sanda 272 Sun Samu Karin Girma A Kano

Daga Mujahid Wada Musa

Rundunar ƴan sandan jihar Kano, ta yi bikin kara wa jami’an ta 272 girma, a matakai daban-daban kamar yadda hukumar kula da aiyukan yan sanda ta kasa PSC ta amince.

An gudanar da bikin karin girman a wajen shakatawar manyan jami’an yan Sanda dake unguwar Bompai a ranar Litinin.

Kwamishinan yan sandan jihar Kano CP Salman Dogo Garba, ya taya wadanda suka samu karin girman, Inda yaja hankalin su kan ci gaba da jajircewa kan aikinsu.

Cikin wadanda likafar ta su ta daga sun hada da, mataimakan kwamishinan yan sanda 4, sai mutane 50 daga matakin SP zuwa CSP sai mutane 32 daga DSP matakin zuwa SP da kuma mutane 286 daga matakin ASP zuwa DSP.

Rundunar ta ce wannan rana ce ta farin ciki agare su, da wadanda suka samu karin girman da kuma iyalansu.

Post masu alaƙa

Tinubu ya sanya hannu kan kasafin kuɗin 2026 na naira tiriliyan 68

Ƙungiyar muhaɗu mugyara ta bayyana Muhasa TVR a matsayin kan gaba wajen gyaran tarbiyyar al’umma.

Fursuna ya tsere bayan hatsarin motar jami’ai a Yobe