‘Yan Sanda Sun Kai Samame Tare da Kwashe Motocin Alfarma a Gidan Tsohon Gwamnan Zamfara

Rundunar ‘yan sanda ta kasa ta kai samame gidan tsohon Gwamnan jihar Zamfara Muhammad Bello Matawalle dake Gusau babban birnin jihar.

Rohotanni sun tabbatar da cewa an gano tare da kwashe motocin alfarma a yayin samamen a gidan tsohon Gwamnan dake rukunin gidajen alfarma na GRA a jiya juma’a.

har yanzu dai ba’a da tabbacin adadin motocin da aka gani a gidan, amma dai wata majiya ta tabbatar da an dauke motocin alfarma guda hudu a gidan 

Kokarin jin tabakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ASP Yazid Abubakar yaci tura.

A kwanakin baya bayan nan Gwamn jihar Zamfara mai ci Dauda Lawal Dare ya zargi Matawalle da kashe tsabar kudi Naira Biliyan biyu da miliyan dari bakwai da casa’in da hudu da dubu Dari uku da talatin da bakwai wajen siyan motocin tawagar gwamna tare da yin awon gaba dasu bayan barin mulki.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr