Home » ‘Yan Sanda Sun Kama ‘Yan Daba 24 Da Muggan Makamai A Kano

‘Yan Sanda Sun Kama ‘Yan Daba 24 Da Muggan Makamai A Kano

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu mutane 24 da ake zargin ‘yan daba ne tare da ƙwato muggan makamai a yayin wani sumame da ta gudanar a tun daga ranakun 13 zuwa 16 ga Disamba, 2024.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ya ce an gudanar da aikin ne da nufin magance tashe-tashen hankula da fadace-fadace tsakanin matasa a yankunan Kofar Mata, Yakasai, Zango anguwar Zage, da kewaye.

Kiyawa ya ce, an tura ‘yan sandan ne bisa umarnin babban sufeton ‘yan sandan Najeriya, IGP Kayode Adeolu Egbetokun domin wanzar da zaman lafiya da tabbatar da tsaro.

Baya ga haka, rundunar ‘yan sandan ta hada hannu da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro da suka hada da Hakimai, ’yan banga, dattijai, da ’yan kasuwa.

An kuma gudanar da gangamin wayar da kan jama’a ta gidajen rediyo da talabijin da kafofin sada zumunta da fata inganta hadin kan al’umma wajen tabbatar da tsaro.

 

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?