Za A Samu Fari A Jihohi 9 Na Arewacin Najeriya A Tsakiya Daminar 2025

Hukumar da ke lura da yanayi a Najeriya NiMet ta yi hasashen cewa za a samu fari mai tsananin gaske a jihohi tara na Arewacin Najeriya a daminar bana. 

Ta ce farin zai iya kai wa tsawon kwanaki 21, a tsakiyar damina daga tsakanin watan Yuni zuwa Watan Agusta a shekarar 2025.

Ana sa ran farin zai shafi jihohin Maiduguri, Gombe, Yobe, Filato, Jigawa, Kano, Zamfara, Sakkwato da kuma jihar Kebbi.

Masana harkokin noma a Najeriya sun shawarci manoma da masu saka hannun jari a fannin noma da su nemi shawarar masana kan yadda ya kamata su yi, domin kaucewa asara mai yawa.

Ko a tsakayar daminar bara ma dai an samu irin wannan fari a jihar Filato, Taraba da wani yanki na jihar Adamawa, abin da ya janyo ƙarancin abinci a kakar bara a waɗan nan yankunan.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya