Ƙaramin ministan tsaro a Najeriya, Bello Matawalle ya ce suna bai wa manoma tabbacin samun isasshen tsaro da zai basu damar komawa gonakinsu gabanin daminar bana domin bunkasa harkokin noma
Ministan ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da manema labarai a garin Maradun, Zamafara, a jiya Lahadi.
Ya ce, an tura jami’an tsaro dazuzzuka domin tabbatar da tsaron filayen noma, kuma ana amfani da fasahar zamani wurin gudanar da aikin.
Ya ce “Muna daukar dukkan matakan da suka dace domin tabbatar da cewa manoma sun koma gonakinsu lafiya tare da cikakkiyar kariya daga duk wata barazanar tsaro a fadin kasar nan,”
- Kungiyar SURE4U Ta Bayar Da Gudunmawar Kayan Aikin Lafiya A Babban Asibitin Hadejia.
- Kwayar Colorado Ta Kashe Dan Shekara 43 A Kwara Yayin Bikin Sallah
Ya kara da cewa, gwamnatin kasarnan na shirin samar da tsarin tsaro na ‘yan asalin yankunan da za su yi aiki domin tunkarar kalubalen tsaro da kuma iya samar da su ga wasu kasashe.
Matawalle ya bukaci gwamnoni su ba da tallafin kayan aiki da suka hada da masauki, motocin aiki, da tattara bayanan sirri, don taimakawa wajen tabbatar da tsaro a yankunan karkara.
Ministan ya ce wasu gwamnonin na yin wasan zargi maimakon goyon bayan kokarin gwamnatin tarayya na magance matsalar rashin tsaro. Kamar yadda Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ta ruwaito
