Zanga-zanga Ce Yaren Da Gwamnati Ke Ji- Dalung

Solomon Dalung

Dan gwagwarmaya kuma tsohon ministan matasa da wasanni, Barista Solomon Dalung ya bayyana cewa za su fara zanga-zanga a yau Alhamis saboda su nuna fushinsu kan yadda ake tafiyar da lamurra a Najeriya.

Barista Solomon Dalung ya tabbatar da cewa zanga-zangar da za su fara ta lumana ce.

Tsohon ministan ya bayyana haka ne a tattaunawarsa da kafar yada labarai ta BBC Hausa.

Dalung ya ce zanga-zanga ce kadai yaren da gwamnati ke ji
“wannan ne yaren da gwamnati ke ganewa kadai.”

Kawo yanzu dai matasan Najeriya sun dage kan aniyarsu ta gudanar da zanga-zangar da suke cewa itace hanyar da za su bi domin bayyanawa gwamnati halin da suke ciki.

Post masu alaƙa

Majalisar Najeriya ta dakatar da zuwa Afirka ta Kudu

Za a miƙa ƴan Najeriya da ake zargi damfara zuwa Amurka

An Kama Masu Safarar Miyagun Ƙwayoyi 7 A Jigawa