Zanga-zanga Ce Yaren Da Gwamnati Ke Ji- Dalung

Solomon Dalung

Dan gwagwarmaya kuma tsohon ministan matasa da wasanni, Barista Solomon Dalung ya bayyana cewa za su fara zanga-zanga a yau Alhamis saboda su nuna fushinsu kan yadda ake tafiyar da lamurra a Najeriya.

Barista Solomon Dalung ya tabbatar da cewa zanga-zangar da za su fara ta lumana ce.

Tsohon ministan ya bayyana haka ne a tattaunawarsa da kafar yada labarai ta BBC Hausa.

Dalung ya ce zanga-zanga ce kadai yaren da gwamnati ke ji
“wannan ne yaren da gwamnati ke ganewa kadai.”

Kawo yanzu dai matasan Najeriya sun dage kan aniyarsu ta gudanar da zanga-zangar da suke cewa itace hanyar da za su bi domin bayyanawa gwamnati halin da suke ciki.

Post masu alaƙa

Tinubu ya cire ministan kuɗi da na gidaje

An kama mutum 2 a hanyar kai wa ’yan ta’adda harsasai 314

Hukumomi a Nijar sun nemi ƴan ƙasar su yi wa jami’an tsaro uziri