Ɗaurarru 16 sun gudu daga gidan yarin Keffi da ke jihar Nasarawa.
Wata sanarwa da Hukumar kula da gidajen gyaran hali ta Najeriya ta fitar ta ce lamarin ya faru da safiyar Talata, kamar yadda mai magana da yawun hukumar ya bayyana.
Sanarwar ta ce wasu daga cikin ɗaurarrun da ke gidan sun ci ƙarfin maʼaikatan da ke tsaron shi, lamarin da ya bai wa mutane 16 damar guduwa nan take.
Hukumar ta kuma ce jamiʼanta biyar da ke sun samu raunuka yayin lamarin, inda biyu daga cikinsu ke cikin mawuyacin hali kuma suna samun kulawa a wani asibitin gwamnati.
Sai dai sanarwar ta ce an yi nasarar kama mutum bakwai daga cikin ɗaurarrun da suka gudu, kuma babban kwanturolan hukumar, Sylvester Ndidi Nwakuche ya ƙaddamar da bincike kan lamarin.