EFCC Ta Saki Tambuwal

Tsohon Gwamnan Sakkwato, Aminu Waziri Tambuwal, ya shaki iskar ’yanci bayan sakinsa da Hukumar EFCC mai yaki da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati ta yi a yammacin wannan Talatar.

A jiya Litinin ce aka ruwaito cewa EFCC ta tsare Tambuwal a hedikwatarta da ke Abuja, inda take zargin ya fitar da wasu kuɗaɗe ba bisa ka’ida ba har naira biliyan 189 a lokacin da yake rike da madafan iko.

 

Post masu alaƙa

An kashe kwamandojin ’yan bindiga biyu a Katsina

NAPTIP ta ceto sama da yara 180 da ake safararsu ta hanyar ƙungiyoyin fara hula na bogi

Nafi’u ya gargaɗi Atiku ya daina sukar Tinubu da sunan ADC