EFCC Ta Saki Tambuwal

Tsohon Gwamnan Sakkwato, Aminu Waziri Tambuwal, ya shaki iskar ’yanci bayan sakinsa da Hukumar EFCC mai yaki da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati ta yi a yammacin wannan Talatar.

A jiya Litinin ce aka ruwaito cewa EFCC ta tsare Tambuwal a hedikwatarta da ke Abuja, inda take zargin ya fitar da wasu kuɗaɗe ba bisa ka’ida ba har naira biliyan 189 a lokacin da yake rike da madafan iko.

 

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda