Ambaliya Ta Karya Gada A Kasar Nijar

Daga Suraj Na Iya Idris Kududdufawa

Babbar gadar da ake shiga babban birnin Yamai a kasar Nijar ta karye sakamakon mamakon ruwa saman da ake yi samu a yankin. 

Gadar ta karye ne tsakanin mahadar jihar Doso da mahadar shiga birnin na Yamai.

Mafiya yawan al’ummar da suke bi ta jihar Doso domin shiga birnin sun hakura da shiga.

A yanzu dai haka akwai motocin matafiya a jibge a hanyar sakamakon wannan lamari da ya afku na karyewar gadar.

Akwai mutane daga jihoshi da dama a kasar Niger da sai sun bi ta jihar Doso sannan su isa birnin suma lamarin ya ritsa dasu.

Post masu alaƙa

Yan sanda sun kama mutane 79 tare da kwato kwayoyi da makamai a bikin Takutaha a Kano.

Yan sanda sun kama wanda ake zargi da damfarar masu neman aikin gwamnati Naira miliyan 40.

Sabuwar majalisar gudanarwa ta POLAC za ta mayar da hankali kan inganta da ilimi da horo.