Hakimin gundumar Jogana da ke ƙaramar hukumar Gezawa ta jihar Kano, Abdulkadir Muhammad Balarabe, ya amince da murabus ɗin wasu masu unguwanni su goma sha uku a ƙasarsa, waɗanda suka yi murabus don ƙashin kansu.
Abdulkadir Muhammad Balarabe, ya bayyana hakan ne a yayi zantawar sa da manema labarai ranar Talata 02 ga watan Satumban 2025, a gundumarsa ta Jogana da ke ƙaramar hukumar Gezawa a jihar Kano.
Abdulkadir Muhammad, ya kuma ce masu unguwannin da suka sauka da kansu, dukkaninsu sun rattaɓa hannu a takarda.
“A cikin takardar sun bayyana cewa sun sauka saboda an kawo ƙarar wani Mai unguwa da yake zaluntar al’ummarsa suka ce indai akayi masa hukunci za su sauka da kuma hakimin ya hukuntashi suka ce sun sauka daga kan mukamansu, in ji shi”.
- Wani Ya Maka ‘Yan Kwamitin Unguwa A Kotu Saboda Sun Hana Shi Zuwa Hira Wurin Bazawararsa.
- ‘Yan Bindiga Sun Sace Hakimin Bagaji Odo a Jihar Kogi
A nasa jawabin shugaban ƙaramar hukumar Gezawa Mukaddas Bala, ya bayyana godiyarsa ga hakimin gundumar Jogana, bisa kokarinsa na tabbatar da gaskiya da adalci, inda ya kuma yi kira ga al’ummar yankin dasu zauna da junansu lafiya.
Rahotanni na cewa, hakimin gundumar garin Jogana Abdulkadir Muhammad Balarabe, ya ce tunda masu unguwanni suka yi murabus don ƙashin kansu, nan bada jimawa ba zaa sake naɗa wasu sababbin masu unguwanni da za su maye gurbinsu.