Gwamnatin Jihar Jigawa ta raba rancen naira miliyan dubu huɗu a matsayin rancen sayen ababen hawa ga ma’aikatan jiha da na kananan hukumomi cikin shekaru uku da suka gabata.
Gwamna Malam Umar Namadi ne ya bayyana hakan yayin jawabi a bikin ranar ma’aikata ta bana, kamar yadda Gidan Rediyon Jihar Jigawa ya rawaito.
Ya ce kimanin ma’aikata dubu goma sha uku ne suka ci gajiyar rancen da nufin inganta rayuwarsu.
A ƙarshe, ya bayyana cewa kula da jin daɗin ma’aikata na aya daga cikin manufofin gwamnatinsa domin sauƙaƙa musu gudanar da aiki yadda ya kamata.