Gwamnatin Jihar Jigawa ta raba rancen naira miliyan dubu huɗu

Gwamnatin Jihar Jigawa ta raba rancen naira miliyan dubu huɗu a matsayin rancen sayen ababen hawa ga ma’aikatan jiha da na kananan hukumomi cikin shekaru uku da suka gabata.
Gwamna Malam Umar Namadi ne ya bayyana hakan yayin jawabi a bikin ranar ma’aikata ta bana, kamar yadda Gidan Rediyon Jihar Jigawa ya rawaito.
Ya ce kimanin ma’aikata dubu goma sha uku ne suka ci gajiyar rancen da nufin inganta rayuwarsu.
A ƙarshe, ya bayyana cewa kula da jin daɗin ma’aikata na aya daga cikin manufofin gwamnatinsa domin sauƙaƙa musu gudanar da aiki yadda ya kamata.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Katsina ta haramta sana’ar POS da cajin waya

Kada ku damu kan batun kafa ’yan sandan jihohi —Sufeto-Janar

Kotu ta umurci INEC ta soke rijistar jam’iyyar ADC