Gwamnatin Jihar Jigawa ta raba rancen naira miliyan dubu huɗu

Gwamnatin Jihar Jigawa ta raba rancen naira miliyan dubu huɗu a matsayin rancen sayen ababen hawa ga ma’aikatan jiha da na kananan hukumomi cikin shekaru uku da suka gabata.
Gwamna Malam Umar Namadi ne ya bayyana hakan yayin jawabi a bikin ranar ma’aikata ta bana, kamar yadda Gidan Rediyon Jihar Jigawa ya rawaito.
Ya ce kimanin ma’aikata dubu goma sha uku ne suka ci gajiyar rancen da nufin inganta rayuwarsu.
A ƙarshe, ya bayyana cewa kula da jin daɗin ma’aikata na aya daga cikin manufofin gwamnatinsa domin sauƙaƙa musu gudanar da aiki yadda ya kamata.

Post masu alaƙa

Ana zargin mahaifi da kashe ’yarsa kan auren dole a Katsina

An kama mutum 2 kan zargin sayar da filayen gwamnatin a Kano

Waɗanda suka sace ɗaliban Oyo sun buƙaci musaya da manyansu muka ƙi’