Ranar Litinin Kwankwaso da Obi za su fice daga ADC – Buba Galadima
Sakatare a kwamitin amintattu na jam’iyyar NNPP kuma jigo a tafiyar Kwankwasiyya, Injiniya Buba Galadima, ya bayyana a ranar asabar cewa ranar Litinin Sanata Kwankwaso da Peter Obi za su fice daga jam’iyyar ADC, Buba Galadima ya kara da cewa za kuma su sanar da sabuwar jam’iyyar da za su koma.
Galadima ya bayyana hakan ne a wani taron masu ruwa da tsaki na tafiyar Obi-Kwankwaso da ya gudana a Abuja