Abdulkarim Chukkol Ya Zama Shugaban Hukumar EFCC Na Wucin Gadi

Abdulkarim Chukkol ya zama mai rikon shugaban hukumar  EFCC, biyo bayan dakatar da AbdurRashid Bawa da shugaban kasa Bola  Ahamad Tinubu yayi.

Sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan yada labarai na ofishin sakataren gwamnati Willie Bassey, da aka fitar a jiya, ta umurci Bawa da ya mika wa daraktan ayyuka na hukumar ta EFCC.

A shekarar 2003 Chukkol ya fara aiki da hukummar EFCC, inda ya kai ga zama babban jami’in bincike da kuma daraktan ayyuka,

Jami’in dan sandan ya taba shugabantar ofishin shiyya na EFCC da ke garin Fatakwal, kafin a mayar da shi hedikwatar hukumar da ke Abuja.

Post masu alaƙa

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM

Gwamnatin Jihar Jigawa ta raba rancen naira miliyan dubu huɗu