Allah ya yi wa sarkin Ebira rasuwa

Allah Ya yi wa Mai martaba Ohinoyi na kasar Ebira, Alhaji Ado Ibrahim rasuwa wanda har ila yau shi ne mataimakin shugaban Jama’atu Nasril Islam (JNI) na kasa,

Dokta Ado Ibrahim ya kasance shahararren dan kasuwa wanda ya shafe yawancin rayuwarsa a jahar Lagas kafin ya zama Ohinoyi na kasar Ebira. Ya hau kujerar sarautar Ohinoyi na kasar Ebira bayan rasuwar Ohinoyi Sanni Omolori na gidan Oziada a shekarar 1997.

An haifi marigayi sarkin ne a ranar 7 ga watan Fabrairun shekarar 1929. Ya yi karatun boko da na addini, ya rasu yana da shekaru 94. Za a yi jana’izarsa a yau lahadi  29 ga watan Oktoba, a fadarsa da ke birnin Okene, a Jihar Kogi.

Post masu alaƙa

Rundunar yan sandan shiyya ta daya ta kama Mutane biyar kan zargin jabun magunguna da sojan Gona.

Kwalejin sojan ruwa dake Dawakin-Tofa ta kara karfafa hadin gwiwar aiki tare da rundunar yan sandan Kano.

Sojojin Najeriya sun ceto mutane 9 daga masu garkuwa a Kogi.