Ambaliya Ta Ɗaiɗaita Dubban Mutane A Valeancia

Tun bayan faruwar ambaliyar ruwa da tayi sanadiyar rasuwar mutane aƙalla 95 tare da raba wasu da muhallan su, ana cigaba da aikin ceto a garin Valeancia dake ƙasar Sifaniya.

Lamarin ya faru a ranar Laraba 30 ga watan Oktoba na shekarar 2024, inda aka shafe awanni shida ana tafka ruwa babu ƙaƙƙautawa. Wannan ita ce ambaliya mafi muni da aka gani a kasar ta Sifaniya.

Zuwa yanzu dai waɗanda suka rasu sun kai aƙalla mutum 95, a daidai lokacin da ake ci gaba da gudanar da ayyukan ceto.

Daga cikin waɗanda suka rasu akwai ɗan Burtaniya mai shekara 71 bayan an ceto shi a gidansa da ke Alhaurin de la Torre a garin Malaga.

Kawo yanzu dai ruwan ya tsagaita, amma firaiministan ƙasar Pedro Sanchez, ya ce akwai buƙatar mazauna yankin su ɗan dakata a tabbatar da tsayawar ambaliyar.

Hukumomi dai a ƙasar sun ce har yanzu ba a tantance haƙiƙanin mutane nawa suke ɓace ba a sanadiyar ambaliyar.

Mutane da yawa sun yi asarar dukiyoyin su da suka haɗa ababen hawa da gidaje dadai sauransu.

Post masu alaƙa

Nafi’u ya gargaɗi Atiku ya daina sukar Tinubu da sunan ADC

Yan Sandan a Kano sun kama mutane 244, ciki har da 117 da ake zargi da fadan daba.

Ƴansanda sun ƙara tsaurara matakan tsaro a bikin Takutaha, tare da gargaɗin masu yunkurin tada zaune tsaye.