Aminu Abdussalam ne ɗantakararmu na gwamna a 2027 – Kwankwaso

Tsohon gwamnan Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya sanar da zaɓar Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo a matsayin wanda zai yi wa jam’iyyar NDC takarar gwamna a zaɓen 2027.

Kwankwaso ya faɗi haka ne a saƙon da ya wallafa a shafinsa na X inda ya ce Dakta Nasiru Yusuf Gawuna kuma zai nemi kujerar sanata don wakiltar al’ummar Kano ta Tsakiya.

Ya ce an ɗauki matakin bisa gaskiya da biyayya da kuma ƙwarewa – ɗabi’un da har yanzu ginshiƙai ne a ci gaba da haɗin kan jam’iyyarmu da kuma Kwankwasiyya.

Saarwar ta zo ne bayan shafe kwanaki ana tattaunawar sirri a tsakanin mambobin Kwankwasiyya da kuma tuntuɓar manyan ƴan siyasa.

Kwamared Gwarzo ya sauka daga muƙaminsa na mataimaki gwamnan jihar Kano a watan Maris sakamakon rikicin siyasa tun bayan da gwamna Abba Kabir Yusuf ya fice daga NNPP ya koma jam’iyyar APC mai mulki.

Post masu alaƙa

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya

Rundunar yan sandan jihar Kano ta kama dan bindiga da sanye da kayan sojoji.

Majalisar Wakilai ta janye kudirinta kan ‘yan sandan jihohi tare da yin nazari kan buƙatar Tinubu