Ba Zan Yi Wa Abba Katsalanda ba a Mulkinsa – Kwankwaso
Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen da ya wuce a Najeriya, Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ce ba zai yi wa gwamnan Kano mai jiran gado, Abba Kabir Yusuf, katsalandan cikin harkokin mulkinsa ba.