NNPC Ta sanar da komawa Haƙar Man Fetur a Jihar Barno

Kamfanin mai na Najeriya NNPC ya sanar da komawa aikin neman mai a yankin Tafkin Chadi da ke jihar Borno.

Kamfanin ya dakatar da aikin ne a watan Yuli na shekara ta 2017, bayan da wasu mahara da ake zargin ‘yan Boko Haram ne suka kai wa ma’aikatan hari har suka yi garkuwa da wasu.

Shugaba Muhammadu Buhari ya gabatar da jawabi ta intanet ga taron kaddamar da komawa kan aikin gano man a wata rijiya da ke yankin Wadi-B a garin Tuba na karamar hukumar Jere.

Kamfanin ya ce yana da kyakkyawan zato cewa za a samu mai da gas mai yawan gaske a wannan wuri.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr