Home » An Ga Watan Ƙaramar Sallah a Najeriya 

An Ga Watan Ƙaramar Sallah a Najeriya 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Mai Alfarma Sarkin Musulmin Najeriya Alhaji Abubakar Sa’ad III ya bayyana cewa an ga watan Shawwal a Najeriya dan haka za a idin ƙamar salla ranar Lahadi. 

Tun da yammacin ranar Asabar ne dai aka bayyana ganin watan Shawwal a ƙasar Saudiyya, kafin daga bisani a samu labarin ganin shi a jamhuriyar Nijar.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi ya bayyana ganin watan ne a fadar sa da ke Sakkwato, Arewa maso yammacin tarayyar Najeriya kamar yadda ya saba.

Kawo yanzu dai ‘yan Najeriya na cigaba da bayyana murnar kammala ibadar watan Ramadan, suna kuma fatan Allah ya karɓa.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?