Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna ta kama wasu mutane 26 da ake zargi da yin garkuwa da mutane, tare da ƙwato bindigogi guda 4, da muggan makamai da dama.
Ta kuma kama wani ɓangare na kuɗin fansa da ake zargin an biya masu garkuwa da mutane a wasu hari daban-daban a jihar.
Nasarar kamen dai ya biyo bayan wasu jerin samame da jami’an ’yan sanda da na ’yan banga suka yi a tsakanin ranakun 3 zuwa 5 ga watan Oktoban 2025, inda suka yi ta kai farmaki kan gungun masu garkuwa da mutane da ke kai hari a ƙananan hukumomin Anchau, Ikara da kuma Makarfi.
Wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan ya fitar a ranar Alhamis, ta ce samamen da aka gudanar tare da haɗin gwiwar hukumar ’yan banga ta Kaduna, wani ɓangare ne na ƙoƙarin kawar da ’yan bindiga da yin garkuwa da mutane a jihar.
- Ban Damu Da Binciken Da Gwamnatin Kano Ke Yi Ba – Ganduje
- Gwamnatin Kano Ta Ce Mutane 2,000 Zata Yi Wa Auren Gata
Sanarwar ta ce, an samu nasarar farko ne a ranar 5 ga watan Oktoba, a lokacin da tawagar ’yan sintiri daga reshen Anchau, da ke aikin sahihan bayanan sirri, suka kai farmaki maɓoyar wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da misalin ƙarfe 1:15 na safe, tare da kama wasu mutane shida da ake zargi da hannu a ciki, ciki har da wani Jibrin Abubakar mai suna Oga, mai shekara 21.
“Bincike ya nuna cewa waɗanda ake zargin sun haɗa baki ne a ranar 22 ga watan Satumba, 2025, don yin garkuwa da wani Idris Adamu mai shekara 60, wanda suka yi garkuwa da shi na tsawon kwanaki kafin su sake shi bayan sun karɓi kuɗin fansa Naira miliyan 5,” in ji Hassan.