Daga: Mohammed Garundole
Allah ya yi wa tsohon Sakataten gwamnatin jihar Borno Marigayi Alhaji Mohammed Kagu Alibe rasuwa da safiyar yau Asabar a asibitin koyarwar Jami’ar Maiduguri.
An gabatar da Sallar Janaizar Alhaji Mohammed Kagu Alibe a gidansa dake old GRA, Maiduguri babban birnin jihar Borno.
Janaizar ta samu halartar Gwamnan jihar Borno Farfesa Baba Gana Umara Zulum da mukarrabansa dakuma tsohon Shugaban Hukumar Shigi da fice ta kasa, kuma Shugaban gidan Radio da talabijin na MUHASA Alhaji Mohammed Babandede OCM OFR.
- Jihar Bauchi Ta Samu Tallafin Riga-kafin Cutar Folio Daga UNICEF
- Kotu Ta Dakatar Da Gangamin Magoya Bayan Wike A Bayelsa
Alhaji Mohammed Kagu Alibe ya rasu yana da shekaru 81, ya bar mata ɗaya Hajiya Aisa k Alibe, da ‘ya’ya biyu biyu da kuma jikoki biyu.
Ya bar yayyu da ƙanne ‘yan uwa da dama.