An Yi Wa Gwamnatin Kano Alqunut Kan Zargin Ƙwace Gonaki

Daga: Safiyanu Haruna Kutama

Al’ummar garin Gano dake karamar hukumar Dawakin Kudu, sun yi wa gwamnatin Kano Al-Qunut, kan zargin ta da yunkurin kwace musu Gonaki.

Mutanen sun gudanar da Sallah tare da yin addu’o’in neman dauki daga Ubangiji.

Magidanta, maza da mata hadi da samari ne suka halarci taron addu’ar daya gudana a safiyar yau Litinin.

Mutanen sun ce gwamnatin tana son kwace musu gonakin da girman su yakai kilomita 5 don yin aiki a wajen. Haka ne yasa al’ummar rokon gwamnatin tayi hakuri ta bar musu filayen su.

Post masu alaƙa

Dubun masu ƙera muggan makamai a Filato ta cika

Dalilin da ya sa na gina Masallatai 50 da aurar da marayu 10 — Mataimakin Gwamna

Dalilin da ya sa zan yi takara – Yusuf Buhari