Mujahid Wada Guringawa

Za mu ƙara ƙaimi wajen daƙile matsalar tsaro — Radda

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ƙara ɗaukar matakan da suka dace domin daƙile matsalar tsaro a faɗin jihar. Radda ya bayyana haka ne bayan kammala sallar Eid-el-Fitr a garin Batagarawa, inda ya ce gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da zaman lafiya da […]

Read more

Shugabannin Turai sun yi wa Trump tawaye kan yaƙin Iran

Karin wasu shugabannin Turai sun yi watsi da buƙatar Shugaban Amurka Donald Trump ta neman taimako wajen tabbatar da tsaron zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigin Hormuz, da Iran ta rufe. Bayan wani taron ministocin harkokin wajen Tarayyar Turai, babbar jami’ar kula da manufofin ƙasashen waje ƙungiyar, Kaja Kallas, ta ce “babu wanda ke son yin […]

Read more

Tinubu ya umarci hafsoshin tsaro su koma Maiduguri

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bai wa hafsoshin tsaro umarnin komawa Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, domin su jagoranci ayyukan tsaro kai tsaye a yankin. Wannan mataki ya biyo bayan hare-haren bama-bamai da suka yi sanadin mutuwar mutane sama da 20 tare da jikkata fiye da 100. Rahotanni daga Maiduguri sun bayyana cewa wasu da […]

Read more

An yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu da Iran a Birtaniya

Ɗaruruwan mutane sun gudanar da zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu a birnin Landan na Birtaniya, duk da cewa gwamnati ta haramta gudanar da gangamin jama’a saboda dalilan tsaro. ’Yan sanda sun ce an kama mutum 12 yayin zanga-zangar, tare da buɗe bincike kan wasu kalaman adawa da Isra’ila da aka yi a wajen gangamin. Ministar harkokin […]

Read more