Mujahid Wada Guringawa

An Gano Gawar Mutane 15 Da Suka Nutse A kwalekwale.

An yi nasarar ceto mutum 26 bayan kifewar wani kwale-kwale a karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja da ke arewa maso tsakiyar Najeriya. Kwale-kwalen na dauke ne da yankasuwa da ke kan hanyar zuwa cin kasuwar Zumba a yankin Kwata a ranar Asabar. Hukumar agajin gaggawa ta jihar Neja ta ce mutum 13 suka mutu […]

Read more

Aikin Gyaran Kundin Tsarin Mulkin 1999 Ba Shi Da Wata Manufa Ta Boye : Sanata Barau Jibrin.

A yayin taron sauraron ra’ayoyin jama’a da ake gudanar a Kano, Mataimakin   Shugaban   majalisar   dattawa   kuma  shugaban kwamitin duba kundin tsarin mulki na 1999, Sanata Barau Jibrin, ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa aikin gyaran kundin tsarin mulki da ake gudanarwa ba shi da wata manufa ta ɓoye, kuma yana gudana ne bisa buƙatun jama’a. […]

Read more

Nentawe Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban APC

Kwamitin zartarwa na Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya, ya amince da nadin Farfesa Nentawe Yilwalda daga jihar Filato a matsayin sabon shugaban jam’iyyar na ƙasa. An cimma matsayar ne yayin taron kwamitin zartarwar na kasa da ya gudana a Abuja. Taron wanda ke gudana a fadar shugaban ƙasar, ya samu halartar Shugaba Bola Tinubu […]

Read more

Sojoji Sun Halaka Yan Bindiga 95 Tare Da Ceto Mutane 138 A Neja

Dakarun Sojin Najeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Ƙananan Hukumomin Rijau da Mariga a Jihar Neja. ’Yan ta’addan sun fito ne daga Jihar Zamfara, yayin da suke tafiya a kan babura ɗauke da muggan makamai. Sojoji tare da taimakon jiragen yaƙi na sama sun kai farmaki bayan samun bayanan sirri. Aƙalla ’yan ta’adda 95 […]

Read more

NAFDAC Ta Gano Sinadaran Haɗa Abubuwan Fashewa A Kano

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta ƙasa (NAFDAC) ta gano wani babban gidan ajiya a Kano da ke cike da sinadarai masu haɗari da ake amfani da su wajen haɗa abubuwa masu fashewa, ciki har da sinadarin sulphuric da nitric acid kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito. Hukumar ta kuma rufe wurin nan […]

Read more