Bayan Kaddamar Da Operation Kukan Kura Jama’a Suna Bayar Da Hadin Kai : Yan Sanda

Rundunar yan sandan jihar Kano ta ya bawa al’ummar jihar bisa hadin kai da goyon bayan da suke basu a koda yaushe don wanzar da zaman lafiya mai dorewa.

cikin wani sako da kakakin rundunar yan sandan jihar Kano , SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya wallafa a shafin sa na Facebook, ya ce mutane suna basu hadin kai sosai wajen taimakawa yan sanda, musamman bayan takaddamar da Operation Kukan Kura wanda ake ta samun nasara a koda yaushe.

A cewarsa acan baya sun taba kaddamar da Operation Puff Adder wato kan kace Kobo, kuma shima jama’a sun bayar da hadin kai sosai, sai dai ya ce a wannan lokaci hadin kan da ake samu yafi na baya.

Post masu alaƙa

Barista Hamza Ɗantani ya jinjinawa CP Bakori da wasu kwamishinonin yan sanda biyu.

Rundunar yan sandan jihar Kano ta ceto fasinjoji 9 bayan musayar wuta da yan bindiga a hanyar Doguwa.

Jigawa ta kaddamar da tsare-tsaren bunƙasa kananan hukumomi 27 na shekaru biyar.