Labarai

Ebola: An dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a Congo

Hukumomi a Jamhuriyar Dimokraiyyar Kongo sun dakatar da zirga-zirgar jiragen sama zuwa yankin Bunia babban binin Ituri har illa masha Allahu, saboda barazanar yaduwar cutar Ebola. Sanarwa daga ma’aikatar sufurin ƙasar ta nuna cewa za a tantance jiragen kayan jin ƙai, da na ma’aikatan lafiya, kuma za a bukaci izini daga hukumomin lafiya da na […]

Read more

Tinubu ya yaba wa gwamnonin APC kan zaɓen fitar da gwani

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bayyana gamsuwarsa kan yadda ya ce gwamnonin ƙasar sun shirya tare da gudanar da zaɓukan fitar da gwani a faɗin jihohisu. Yayin da yake jawabi a mazaɓarsa ta Ikoyi bayan ya halarci zaɓen, Shugaba Tinubu ya ce ya ji daɗin yadda zaɓen ke tafiya cikin lumana kamar yadda aka tsara. […]

Read more

Ɗan Ganduje Ya Sayi Fom Ɗin Takarar Majalisar Tarayya A NDC

Abdulaziz Umar Ganduje, babban ɗan tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya sayi fom ɗin takarar kujerar Majalisar Tarayya a ƙarƙashin jam’iyyar NDC. Zai tsaya takarar ne a mazaɓar Dawakin Tofa/Tofa/Rimin Gado da ke Jihar Kano. Duk da kasancewar mahaifinsa a jam’iyyar APC, Abdulaziz, ya daɗe yana bin siyasar Kwankwasiyya kuma yana […]

Read more

Hukumar tsaron farin kaya ta Civil Defence  (NSCDC) reshen jihar Gombe, ta kama wasu mutane biyar da ake zargi da hannu a ƙungiyoyin satar babura da na’urorin lantarki a sassa daban-daban na jihar. Kamen ya biyo bayan wasu samame da jami’an hukumar suka gudanar bisa bayanan sirri a ƙananan hukumomin Billiri da Balanga da Akko […]

Read more

Daraktan yaɗa labaran DHQ Manjo Janar Samaila Uba, ya bayyana cewa a yaƙin haɗin gwiwa da dakarun Najeriya da kuma sojojin Amurka na AFRICOM suna cin galabar ‘yan ISIS. Manjo Janar Sama’ila Uba ya bayyana hakan ne a jiya Talata a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja.

Read more

CP Bakori ya gana da masu ruwa da tsaki kan tsaro a Tudunwada.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya kai ziyarar duba halin tsaro da ganawa da al’umma a yankin Tudun Wada domin karfafa hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da jama’a. Ya ce ziyarar ta bashi damar samun bayanai kai tsaye kan halin tsaro a kananan hukumomin, Tudun Wada da Doguwa da Sumaila da Kiru, […]

Read more